An Shigar Da Kararraki 807 Kan Zaben Najeriya

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya INEC, Farfesa Mahmud Yakubu

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya INEC, Farfesa Mahmud Yakubu

Hukumar zaben Najeriya ta INEC, ta ce an shigar da kararraki 807 a kotunan karar zabe, biyo bayan zaben 2019 da a ka gudanar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a taron karshe na kwamishinonin hukumar na jihohi.

A cewar shi, cikin adadin kararraki 807 an kori 582, masu kara kuma sun janye 183.

Farfesa Yakubu ya ce bisa hukuncin kotu, hukumar zaben za ta sake zabe a mazabun wasu ‘yan majalisar dattawa, da wakilai da suka kai 30.

Jami’in yada labaran hukumar, Aliyu Bello, ya ce kararrakin ba sabon abu ba ne, in an duba zabukan baya.

A ra'ayin masanin kimiyyar siyasa na jami’ar Abuja Dr.Farouk B.B Farouk, da wuya a samu hujjar kalubalantar zabe a kotu.

Saurari rahoto cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

An Shigar Da Kararraki 807 Kan Zaben Najeriya