An kai Harin Kunar Bakin Wake a Jami’ar Maiduguri.

  • Ladan Ayawa

Mutane suka hallara a wurin da aka kai harin kunar bakin wake a jalingo, a jihar Taraba.

A cikin daren jiya Lahadi, da musalin kafe 10 zuwa goma da rabi ne wakilin sashen Hausa Haruna Dauda Biu yace suka dinga samun kira daga jamaa daban-daban daga sassan birnin Maiduguri.

Mutanen suka ce suna jin karar fashe-fashe da kamar tashin boma-bomai da harbe-harbe a wajen tashar Bama.

Kuma ana kyautata zaton cewa ‘yayan kungiyar Boko Haram ne suka kawo hari a wannan yanki.

Harunan yace amma daga bisani sun samu gaskiyar bayanin cewa yan kungiyar boko haram ne kamar yadda suka saba gudanar suka gudanar da wannan hare-hare sun kai hari cikin jamiaar Maiduguri.

Ance wadannan yan kunar bakin waken sunje wajen ofishin jamiaan tsaro na jamiar.

Ga dai Haruna Dauda da cikakken bayani.1’29

Your browser doesn’t support HTML5

An kai Harin Kunar Bakin Wake a Jami’ar Maiduguri. 1'29