An Cimma Jituwar Kwance Damara Tsakanin Gwamnatin Sudan Ta Kudu Da 'Yan Tawaye

  • Ibrahim Garba

Shugaban Sudan Ta Kudu Salva Kiir

A wani al'amarin da wasu za su ce ba girin-girin ba ta yi mai, Gwamnatin Sudan Ta Kudu da 'yan tawaye, bayan gwabzawar da aka yi ta yi, sun cimma yarjajjeniyar tsagaita wuta tare da cigaba da aiwatar da wasu matakai na yada zaman lafiya tsakaninsu.

Gwamnatin Sudan Ta Kudu da kungiyoyin mayaka sun rattaba hannu kan yarjajjeniyar tsagaita wuta jiya Alhamis, a yayin tattaunwar zaman lafiya a kasar Habasha, a yinkurinsu na baya-bayan nan na kawo karshen yakin basasar da aka kwashe shekaru hudu ana yi.

Yarjajjeniyar ta tanaji cewa zuwa gobe Asabar dukkan bangarorin za su kawo karshen gwagwarmaya da makami, su janye daga fagen daga, su saki fursunonin yaki, da ‘yan siyasan da ke tsare, da kuma mata da yaran da aka kama.

Ciyaman din Kungiyar Tarayyar Afirka Moussa Faki ya bayyana yarjajjeniyar da abin da ya kira, “matakin farko mai karfafa gwiwa,” a kokarin da ake na kawo karshen yakin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da muhallansu.