A Soma Duba Wata Daga Yau Asabar Inji Fadar Sarkin Musulmi Ta Sokoto

sabon wata

Shugaban kwamitin bada shawarwari kan sha'anin addini Farfesa, Sambo Waleed Junaidu ne ya sanyawa sanarwar hannu

Majalisar Sarkin Musulmi Abubakar Saad na uku ta fitar da sanarwa game da lokacin da ya kamata a fara neman ganin watan sallar azumi.

Wakilin Sashen Hausa a Sokoto Murtala Faruk Sanyinna yayi karin bayanin sanarwar a wata tattaunawa da babban editan Sashen Hausa Aliyu Mustapha.

Your browser doesn’t support HTML5

Daga daren yau asabar za a fara neman ganin watan Sallah - 2':49"

Kafin sanarwar ta Fadar Sarkin Musulmi tuni har mutane sun fara aikawa juna da wasu sakonni masu rudarwa game da ganin watan na sallar azumi.