'Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Kan Kwambar Ado Bayero

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero

Jami'ai suka ce mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, bai ji rauni ba a lokacin da aka kai farmaki a kan kwambar motocinsa asabar din nan.
Wasu 'yan bindiga a Najeriya sun kai farmaki a kan kwambar motocin daya daga cikin manyan shugabannin Musulmi na kasar, suka kashe mutane uku.

Jami'ai suka ce mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, bai ji rauni ba a lokacin da aka kai farmaki a kan kwambar motocin nasa asabar din nan.

Ya zuwa yanzu, babu wanda ya dauki alhakin kai wannan hari a birnin Kano, birni mafi girma a yankin arewacin Najeriya.

Wannan lamari ya faru ana saura kwana daya tak a cikia shekara guda da mummunan harin bama-bamai da harbe-harben da ya kashe mutane 184 a birnin na Kano. An dora laifin harin na bara a kan kungiyar nan ta Boko Haram.

Kungiyar ta Boko Haram tana ikirarin cewa tana gwagwarmayar bkafa dokokin Shari'a ne a fadin Najeriya, kasar da akasarin mutanen arewacinta Musulmi ne, yayin da Kirista suka fi rinjaye a kudu.