Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zanga Zanga Ta Rikide Zuwa Tashin Hankali A Wasu Sassan Burtaniya Bayan Kisan Wasu Yara 3


ISRAEL-PALESTINIANS/PROTESTS-BRITAIN
ISRAEL-PALESTINIANS/PROTESTS-BRITAIN

Masu zanga-zanga sun kai hari kan 'yan sanda tare da tada wuta a birnin Sunderland da ke arewa maso gabashin Burtaniyya a ranar Juma'a yayin da tashin hankalin ya bazu zuwa wani garin a arewacin kasar, biyo bayan kisan wasu yara uku a ranar Litinin a Southport.

Masu zanga-zangar nuna kyamar baki sun jefi ‘yan sanda da duwatsu a kusa da wani masallaci a birnin, kafin daga baya suka jirkitar da motoci, suka cinna wa wata mota wuta sannan suka tayar da wuta a kusa da wani ofishin ‘yan sanda, kamar yadda kafar yada labaran BBC ta bayyana.

“Tsaro da kariyar jama’a su ne babban abin da muka sa a gaba, kuma da muka gano cewa an shirya zanga-zanga, mun tabbatar da cewa an kara yawan jami’an ‘yan sanda a cikin birnin,” a cewar shugabar ‘yan sandan Northumbria, Helena Barron a cikin wata sanarwa.

"Da maraicen Juma’a wadannan jami'an sun gamu da mummunan tashin hankali wanda abin takaici da Allah wadai ne," a cewar Barron.

Shugabar ‘yan sandan ta kara da cewa an kwantar da jami'an 'yan sanda uku a asibiti, kuma an kama mutane takwas bisa laifukan da suka hada da tada zaune tsaye da kuma sata.

Zanga-zangar da aka yi a Sunderland na daya daga cikin wasu fiye da goma sha biyu da ‘yan rajin kyamar baki suka shirya a fadin Birtaniya a karshen mako, ciki har da a kusa da akalla masallatai biyu a birnin Liverpool, birnin da ke kusa da inda aka kashe yaran.

Haka kuma, an shirya yin zanga-zangar adawa da kyamar baki a wurare da dama.

Jami'ai sun ce an baza 'yan sanda a fadin kasar a ranar Juma’a kuma masallatai sun dauki tsauraran matakan tsaro.

Ana tuhumar wani matashi dan shekara 17 da laifin kisan yaran (mata) uku a wani hari da wuka a wani wurin koyar da rawa a garin Southport da ke arewa maso yammacin kasar, lamarin da ya girgiza al’ummar kasar.

Abubuwan tada hankali sun faru a cikin kwanakin da suka biyo baya a Southport, da garin Hartlepool, da kuma birnin Landan a matsayin martani ga bayanan karya da aka yada a shafukan sada zumunta, wadanda ke ikirarin cewa wanda ake zargi da harin wukar bako ne mai tsattsauran ra’ayin addinin Islama.

A wani yunkuri na kawar da ikirarin, 'yan sanda sun jaddada cewa matashin da ake zargi a Biritaniya aka haife shi.

A ranar ta Juma'a, Firai Minista Keir Starmer ya kai ziyara karo na biyu a Southport tun bayan kisan.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG