Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

USAGM: Hukumar Kula Da kafofin Yada Labarai Na Radiyo Da Talabijin Na Kasar Amurka Ta Gudanar Da Taron Kiwon Lafiya Wa ‘Yan Jarida


USAGM
USAGM

Hukumar dake kula da Kafofin yada labarai na Radiyo da Telabijin na Kasar Amurka a Najeriya ta gudanar da taron bita wa ‘yan jarida masu bada rahoto game da harkokin kiwon lafiya, a jihar Bauchi.

BAUCHI, NIGERIA - Taron na da zummar fahimtar da su game da sabbin hanyoyin gano matsalolin da ke shafar al’umma a fannin cututtuka iri daban daban, don bada rahotanni a kansu.

A taron bitar na tsawon kwanaki uku, an gayyato 'yan jarida daga gidajen radiyo guda biyu da suka hada da BRC Bauchi wanda mallakar Jiha ne, sai kuma gidan radiyon Albarka Radiyo, wanda mai zaman kansa ne, sai kuma gidan Talabijin na BATV, wanda mallakar Jihar Bauchi ne.

Kwararren dan Jarida kan sha’anin harkar kula da lafiya, kuma malami a jami’a a Jihar Legas, Declan Ohenacho, ya bayyana karfin gwiwarsa, kan irin 'yan jaridun da suka halarci taron bitar, inda ya ce an aza harsashin juyin juya hali kan yadda za a rinka bada rahotannin kiwon lafiya a Jihar.

Ya ce sakonsa ga gidajen yada labarai shi ne, su bada dukkan goyon baya wa ‘yan jarida dangane da irin ayyukan da suke son gudanarwa, domin kuwa suna da kwarrarun ma’aikata ‘yan jarida, abin da suke bukata shi ne yanayi mai kyau da goyon baya don gudanar da ayyukansu.

Jami’in da ke wakiltar, hukumar gidajen Radiyo da Telebijin na Amurka a Najeriya, Alhaji Sani Muhammed, ya yi Karin haske kan abubuwa da dama akan batun Bitar.

Mahalarta taron sun yi bayanin irin alfanun da suka samu a sakamakon halartar bitar.

Saurari rahoton Abdulwahab Muhammad:

USAGM: Hukumar Kula Da kafofin Yada Labarai Na Radiyo Da Talabijin Na Kasar Amurka Ta Gudanar Da Taron Kiwon Lafiya Wa ‘Yan Jarida.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:31 0:00

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG