Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Zai Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Ga Majalisar Dokokin Najeriya A Gobe Talata


Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya bayyana hakan yayin zaman Majalisar.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gabatar da kudirin kasafin 2025 a gaban Majalisun Dokokin kasar a gobe Talata.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya bayyana hakan yayin zaman Majalisar.

Kasafin na 2025 zai kasance cikakken kasafi na 2 da Shugaba Tinubu zai gabatarwa Majalisun Dokokin Najeriya tun bayan hawan kan karagar mulki a watan Mayun 2023.

A jawabinsa, Akpabio yace za’a fara gabatar da kasafin kudin din ne da misalin karfe 11 na safiya a zauren Majalisar Wakilai.

A ranar 3 ga watan Disamban da muke ciki, Majalisar Dattawan ta amince da dokar kashe kudade mai matsakaicin zango (MTEF) ta tsakanin 2025 zuwa 2027 da tadabarun sarrafa kudade(FSP) da jumlarsu ta kai Naira tiriliyan 47.9.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG