Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu, Obi Sun Taya Tems Murnar Lashe Kyautar Grammy


Tems
Tems

Tems wacce ainihin sunanta shine Temilade Openiyi ta lashe kyautar fitacciyar waka daga nahiyar Afrika mai taken “love me jeje,” inda tayi takara da mawakan Najeriya irinsu Davido da Yemi Alade da Asake da Wizkid da Lojay da kuma Burna Boy.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu da Peter Obi sun jinjinawa mawakiya Tems saboda nasarar da ta samu a karo na 67 na bikin ba da kyaututtukan “Grammy” da safiyar yau Litinin.

Sa’o’i bayan lashe kyautar, Shugaba Tiinubu ya bayyana nasarar da wacce ta dace.

“A madadin gaba dayan kasarmu, Shugaba Tinubu ya yabawa mawakiyar game da baiwar fasaha da Allah yayi mata, wacce ta sanya Najeriya alfahari a idon duniya har sau 2,” kamar yadda mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya bayyana a sanarwar daya fitar da maraicen yau Litinin.

Tems wacce ainihin sunanta shine Temilade Openiyi ta lashe kyautar fitacciyar waka daga nahiyar Afrika mai taken “love me jeje,” inda tayi takara da mawakan Najeriya irinsu Davido da Yemi Alade da Asake da Wizkid da Lojay da kuma Burna Boy.

A cikin sakonsa na taya murna, Peter Obi yace ako da yaushe irin dimbin nasarar da matasan Najeriya ke samu a fannoni daban-daban na rayuwa na faranta masa rai, musamman ma a bangaren nishadi.”

“Don haka anan ina mika sakon taya murna ga tauraruwar kidan Afrobeat ta Najeriya, Tems, wacce ta lashe kyautar Grammy a karo na 2 a rukunin mafificiyar waka daga nahiyar Afrika,” kamar yadda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben Najeriya na 2023 ya wallafa a shafinsa na X da safiyar yau Litinin.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG