Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Turkiyya Sun Kai Harin Martani Akan 'Yan tawayen Kurdawa


Sojojin Turkiyya
Sojojin Turkiyya

Harin ya zo ne bayan sa’o’i kadan da ake zargin 'yan tawaye Kurdawa sun ta da bama-bamai da kuma bude wuta a kamfanin sararin samaniya da tsaro na TUSAS.

Sojojin saman Turkiyya sun kai hari kan wuraren mayakan 'yan tawaye na Kurdawa a Iraqi da Syria a matsayin martani ga wani hari da aka kai a wani kamfani mai kula da tsaro na gwamnati.

Harin ya yi sanadiyar mutuwar mutum biyar da kuma jikkata fiye da mutum 20.

Ma’aikatar tsaron kasar ta bayyana cewa an "lalata" wurare fiye da 30 a wannan farmaki na sama, ba tare da yin cikakken bayani game da wuraren da aka kai harin ba.

Harin ya zo ne bayan sa’o’i kadan da ake zargin 'yan tawaye Kurdawa sun ta da bama-bamai da kuma bude wuta a kamfanin sararin samaniya da tsaro na TUSAS.

Ministan cikin gida, Ali Yerlikaya, ya ce maharan biyu — namiji da mace — su ma sun mutu.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG