Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabanci: Majalisar Dattawa Ta Sake Gaurewa Da Takaddama


Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki
Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki

Yayin da Majalisar Dattawan Najeriya ke jiran sunayen Ministoci daga Fadar Shugaban kasa, Majalisar ta sake gaurewa da rigimar Shugabaci

Bayan dawowa daga hutu, zaman farko na Majalisar Dattawan Najeriya ya gaure da zafaffiyar muhawara wadda ke da nasaba da shugabancin Majalisar Dattawan. Gardama ta fara barkewa ne tsakanin Shugaban Majalisar Dattawan Abubakar Bukola Saraki da kuma Sanata Kabiru Marafan Gusau.

Wakiliyarmu a Majalisar Dattawan Madina Dauda ta ce hatsaniyar ta faru ne bayan da Shugaban Majalisar Dattawan ya yi jawabin maraba, inda Sanata David Umaru na APC daga jahar Naija ya nemi ya gabatar da kudurin nuna goyon baya ga Shugaban Majalisar saboda, a ta bakinsa, a samu natsuwa da kuma damar yi ma jama’a aiki, inda shi kuma Sanata Kabiru Marafan Gusau ya ce sam.

Bayan hatsaniyar, ‘yan’majalisa tamanin da uku sun kada kuri’ar amincewa da shugabancin Shugaban Majalisar. A halin da ake ciki kuma, da Madina ta tambayi mai magana da yawun Majalisar Dattawan Sanata Dino Melaye ko an sami wasika daga Fadar Shugaban kasa sai ya ce lallai sun sami wasiku daga Fadar Shugaban kasa. Akwai wasikar nada Babban Ciyaman na hukumar FRIS, da kuma ta nada babban manajan AMCON da kuma ta nada Mataimakin Babban Ciyaman na Hukumar Sadarwa Ta Kasa kuma daga gobe za su fara aiki a kansu. Ya ce daga yanzu zuwa dare sun a kyautata zaton za a samu sunayen Ministoci daga Fadar Shugaban kasar.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:18 0:00
Shiga Kai Tsaye

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG