Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

PDP Za Ta Sake Gudanar Da Zaben Fitar Da Gwani A Jihar Bauchi


Gwamnan Bauchi Bala Mohammed (Kauran Bauchi)
Gwamnan Bauchi Bala Mohammed (Kauran Bauchi)

Rahotanni daga jihar Bauchi, na nuni da cewa za a sake zaben ne bayan da dan takarar da aka zaba ya janye.

Jam’iyyar PDP din ta bayyana hakan ne biyo bayan da gwamnan jihar Bala Abdulkadir Muhammed, ya sha kaye a zaben fitar da gwani na takarar kujerar shugaban kasan Najeriya da aka gudanar a makon da ya gabata a Abuja.

Idan za’a iya tunawa dai a karshen makon daya gabata ne Jam’iyar PDP, mai mulki a jihar Bauchi ta gudanar da zaben fidda gwani don yin takarar kujerar gwamnan jihar, inda aka zabi, tsohon sakataren gwamnatin jihar, Barrister Kashim Ibrahim, a matsayin wanda zai yi takara.

Amma kuma sai ga shi kasa da sati guda da gudanar da zaben fitar da gwanin, wanda aka zaba Barrister Ibrahim Kashim, ya ce ya ajiye wannan takara don kashin kansa, kuma gwamna mai-ci, Sanata Bala Abdulkadir Muhammada, shi ne zai yi takarar kamar yadda kakakin jam’iyar PDP din a Jihar Bauchi ya shaida mana.

A gefe guda kuma masu nazarin harkar siyasa, sun ce ba sa mamakin faruwar hakan, a cewar wata ‘yar siyasa Hajiya Ladi da ta shaida mana ta wayar tarho.

A halin da ake ciki kuma, ‘ya’yan babban Jojin Najeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, su biyu sun samu nasara a zaben fitar da gwani, a shiyyar Bauchi ta Arewa, inda guda ya samu nasarar zaben fitar da gwanin a matsayin dan majalisar wakilai a jam’iyar PDP, a yayin da dayan kuma ya samu nasara don yin takarar kujerar Sanata, a Jam’iyyar APC.

Kakakin jam’iyar PDP, a jihar Bauchi ya tabbatar mana da nasarar da dan jam’iyar tasu ya samu.

Saurari rahoto cikin sauti daga Muhammad Abdulwahab:

Jam’iyyar PDP Za Ta Sake Gudanar Da Zaben Fidda Gwani A Jihar Bauchi
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:13 0:00

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG