Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Dau Matakin Rage Radadin Janyewar Tallafin Amurka


Hukumar USAID Ta Kuduri Aniyar Tallafawa Wasu Jihohin Nijar
Hukumar USAID Ta Kuduri Aniyar Tallafawa Wasu Jihohin Nijar

Duk da jinkirta matakin a wasu fannoni, har yanzu akwai fargaba akan abin da zai kasance nan gaba a bangaren tallafin da Amurka ke bayarwa a fannin lafiya a fadin duniya.

Jami’an gwamnatin Najeriya sun kafa wani kwamitin da zai samar da wani tsari mai dorewa wanda zai maye gurbin Shirin tallafin lafiyar da asususun raya kasashe masu tasuwa USAID yake daukan nauyinsu biyo bayan matakin Trump na dakatar da shirye shiryen asusun tallafin na tsawon kwanaki 90. Manufar kwamitin da ya kunshi ministoci daban daban ita ce tabbatar da ya samo tallafin kudin da za su tallafa wa shirye shiryen lafiya masu mahimmaci.

Wakilin Muryar Amurka a Abuja, Timpothy Obiezu, ya ba da rahoton cewa, ministan lafiyar Najeriya y ace kwamitin ya kunshi jami’ai daga ma’aikatar kudi, lafiya da muhalli, domin tabbatar da cewa masu shan maganin HIV, tarin fuka da malariya ba su fuskanci wata komabaya ba yayin da ake fuskantar rashin tabbas akan dokokin Amurka.

Bada jimawa ba bayan da ya karbi ragamar mulki makonni 2 da suka gabata, Shugaban Amurka Donald Trump ya bada umurnin dakatar da ayyukan tallafin Amurka tsawon kwanaki 90. Sai dai ‘yan kwanaki bayan nan, ya amince da ci gaba da bada tallafin wucin gadi don ceton rai a bangaren agajin jinkai, da suka hada da magunguna, kulawar lafiya, abinci da muhalli.

Duk da wannan matakin, har yanzu akwai fargaba akan abin da zai kasance nan gaba a bangaren tallafin da Amurka ke bayarwa a fannin lafiya a fadin duniya.
Najeriya tana doga cikin kasashen da suke samun tallafi mai tsoka daga tallafin da Amurka ta ke bai wa kasashen waje, inda a 2023 ta samu tallafin dalar Amurka biliyan $1.02, galibi daga hukumomi irin su USAID.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG