Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ministan Ilimin Nigeria Ya Umurci Jami'oi Da su Bada Ilimi Mai Inganci


Ministan ilimin Nigeria Malam Adamu Adamu ya bukaci jami’oin Nigeria da su dage da baiwa dalibai ilimi mai inganci, domin samar da dalibai masu kwazo da basira.

Malam Adamu Adamu da shugaban jami’ar tarraya dake Oye Ekiti, Prof. Kayode Shoyemekun ya wakilta yayi kiran ne a lokacin da yake gabatar da jawabin ministan a wani taro a Oye Ekiti. Malam Adamu ya ce don samar da ingantacen ilimi da kuma kwarewa yana kira ga jami’o'in kasar da samar da dalibai suke da kwarewa da basira da kwazo.

A nasa jawabin sakataren hukumar dake kula da jam’ioin Nigeria, NUC a takaice, Prof Rashid Abubakar wanda daraktan hukumar Dr. Chris Maiyaki ya wakilta ya ce suna daukan matakai kan jami’oin gwamnati da masu zaman kansu a Nigeria domin tabbatar suna bada ilimi mai inganci da nagarta.

Sakataren NUC Rashid Abubakar ya shawarci iyaye da su yi hulda da jami’oin da hukumar NUC ta tanttance a fadin Nigeria. A nasa bangaren shugabn taron mai mukamin sarautar gargajiya ta Oni of Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi, ya bukaci daliban Nigeria da su rungumi tarbiya mai kyau wajen gina kasa.

Ministan Ilimin Najeriya Ya Umurci Jami'oi Da Su Bada Ilimi Mai Nagarta 2'16
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:15 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG