Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Indiya Na Daukar Matakan Binciken Shari'ar Fyade cikin sauri


Masu zanga zanga kan fyade
Masu zanga zanga kan fyade

Kotun kuma ta ce ya kamata a samar da manyan kotuna da su ka yi tanade-tanade don yara.

Kotun kolin kasar India ta ba manyan kotunan kasar umurnin gudanar da bincike cikin sauri akan fyaden yara, a daidai lokacin da jama’a ke nuna fushinsu akan fyade da kashe-kashen yara mata da kuma wasu hare-haren akan yara kanana da aka yi kwanan nan.

Babban alkalin kotun kolin kasar, Dipak Misra, ya bada umurnin a kafa kwamiti na binciken gaggwa don binciken kararraki cikin sauri, kuma a wasu kotuna na musamman za a yanke hukuncin.

Yayinda rikicin siyasa a India ya yi kamari akan yawan fyade da kisan yara kanana, a watan da ya gabata, gwamnatin kasar ta amince da hukuncin kisa akan duk wadanda aka samu da laifin yiwa yara ‘yan kasa da shekaru 12 fyade.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG