Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumomin Senegal sun saki mutane 4 da aka zarga da kulla makarkashiyar juyin mulki wa shugaba Abdoulaye Wade


Abdoulaye Wade (File photo)
Abdoulaye Wade (File photo)

Hukumomin Senegal sun saki mutane 4 da aka zarga da kulla makarkashiyar juyin mulki wa shugaba Abdoulaye Wade, su na masu fadin cewa babu wata kwakkwarar shaidar da zata sa a ci gaba da rike su. Kakakin gwamnati, Moustapha Guirassy, ya fada jiya talata cewa a bayan binciken farko da aka gudanar, ba a ga wata shaida tartibiya cewa mutanen su na shirya juyin mulki ba.

Hukumomin Senegal sun saki mutane 4 da aka zarga da kulla makarkashiyar juyin mulki wa shugaba Abdoulaye Wade, su na masu fadin cewa babu wata kwakkwarar shaidar da zata sa a ci gaba da rike su. Kakakin gwamnati, Moustapha Guirassy, ya fada jiya talata cewa a bayan binciken farko da aka gudanar, ba a ga wata shaida tartibiya cewa mutanen su na shirya juyin mulki ba. Guirassy yace an saki mutanen daren litinin, koda yake yace har yanzu ba a rufe wannan batun ba. A ranar asabar ne ministan shari’a na Senegal, Cheikh Tidiane Sy, ya fada ta gidan telebijin na kasar cewa mutanen sun so kai hare-hare kan wasu cibiyoyi, ciki har da wata kasuwa dake cika da mutane a tsakiyar birnin Dakar. Wannan sanarwa ta zo jim kadan kafin dubban mutane su yi zanga-zangar nuna kin jinin shugaba Wade da kuma munin yanayin rayuwa a birnin na Dakar. ‘Yan zanga-zanga da yawa sun ce zargin da gwamnatin ta yi cewa ana kulla makarkashiyar juyin mulki, wani yunkuri ne kawai na share kafar wannan zanga-zanga. An yi wannan zanga-zanga a ranar cikar shekaru 11 da hawan shugaba Wade kan mulki. An yti zanga-zangar a dandalin ‘yanci na Dakar, dandalin da masu zanga-zangar suka yi wa lakabi da sunan Tahrira, watau sunan dandalin nan na al-Qahira da ya zamo cibiyar masu tunzurin da suka kawar da shugaban Masar daga kan mulki.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG