Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumomin Najeriya Sun Ayyana Laraba Ranar Hutun Mauludi


Wasu da suka mahalarta taron Maulidi a birnin Jos a jihar Filato (Hoto: Facebook/Bashcology-Bash)
Wasu da suka mahalarta taron Maulidi a birnin Jos a jihar Filato (Hoto: Facebook/Bashcology-Bash)

Gwamnatin tarayya ta bayyana ranar Laraba, 27 ga watan Satumba, a matsayin ranar hutu domin gudanar da bikin Mauludi (Eid-El-Maulud) da Musulmai ke yi domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad S.A.W.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, Sakataren dindindin na ma’aikatar cikin gida, Dokta Oluwatoyin Akinlade, ya bayar a madadin, ministan harkokin cikin gida, Hon Olubunmi Tunji-Ojo, ya taya daukacin al’umar Musulmi murnar zagayowar wannan rana.

Ya kuma yi kira gare su, da su kasance masu nuna hakuri da juriya wadanda suna daga cikin dabi’un Manzon Allah S.A.W.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ministan na taya daukacin al’ummar Musulmi na gida da na kasashen waje murnar riskar bikin na bana.

Eid-ul-Maulud biki ne da Musulmi ke yi a duk shekara don nuna murna ga zagoyar wannan rana.

Bikin na Maulidi na dauke da tarukan wa’azi, da addu’o’in yabon Manzon Allah S.A.W., karatun al-Qur'ani da kuma yin sadaka.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG