Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hillary Clinton Tana Yiwa Kwamitin Majalisar Amurka Bayani


Hillary Clinton tana isa majalisar dokokin Amurka domin yin bayani. Washington, D.C., Oct. 22, 2015
Hillary Clinton tana isa majalisar dokokin Amurka domin yin bayani. Washington, D.C., Oct. 22, 2015

Yanzu haka tsohuwar Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton ta soma gabatarda bayanai a gaban wani kwamitin musamman na ‘yanmajalisar dokokin Amurka.

Kwamitin da akace ‘yan jam’iyyar dake adawa da ita ta Republicans ne ke da rinjaye akansa, wanda kuma yake gudanarda bincike akan harin da aka kai akan opishin jakadancin Amurka a birnin Benghazin Libya a shekarar 2012.

Ana sa ran Ms. Clinton zata wuni tana bada bayanai masu yawa dangane da wannan farmakin da aka kai ran 11 ga watan Satumban 2012 din,inda a ciki aka kashe tsohon jakadan Amurka Christopher Stevens da wasu Amurkawa guda ukku – kuma wannan ta faru ne a lokacinda ita Hilary Clinton take kan mukamin Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka.

Sai dai Ms. Clinton tana bayyana a gaban majalisar dokokin ne a daidai lokacinda ake ta zargin ‘yan jam’iyyar ta Republicans akan cewa sun suna anfani da wannan bincike ne don kawo cikas ga kokarin da Ms Clinton ke yi na zama ‘yar takarar shugaban kasa ta jam’iyyar Democrats a zaben 2016.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG