Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al’ummar Rivers Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Malalar Mai


Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da suka rubuta korafe-korafensu.

Al’ummar garin Ogale dake karamar hukumar Eleme ta jihar Rivers sun gudanar da zanga-zanga a kan matsalar malalar mai da suke zargin reshen kamfanin mai na Shell da haddasawa.

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da suka rubuta korafe-korafensu.

Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

A ranar 5 ga watan Fabrairun da muke ciki reshen kamfanin Shell na Najeriya ya ba da rahoton samun malalar mai a Ogale, kusa da birnin Fatakwal, lokacin da wani ramin tattara dagwalo ya yi ambaliya yayin aikin wanke bututu.

Masu zanga-zanga a jihar Ribas
Masu zanga-zanga a jihar Ribas

Kamfanin ya kara da cewa tawagar karta kwana a kan malalar ta yi martani tare da tsayar da ambaliyar da kuma sanar da hukumomi, inda ya kara da cewa ana tsare-tsare a kan yadda wata tawaga karkashin jagorancin masu sanya idanu za ta nazarci musabbabi da kuma tasirin malalar man.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG