Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

A Fara Duban Watan Ramadan Daga Yau Lahadi - Sarkin Musulmi


Sarkin Musulmi Muhammadu Sa'ad Abubakar III
Sarkin Musulmi Muhammadu Sa'ad Abubakar III

A Najeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, kuma Shugaban Majalisar Koli ta Addinin Musulunci, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar (III), ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su fara duban watan azumin Ramadan daga yau Lahadi.

Sarkin Musulmi Abubakar, ya yi wannan kiran ne a wata takardar bayani mai dauke da sa hannun Farfesa Sambo Junaidu, Ciyaman din Kwamitin Bayar Da Shawarwari kan harkokin Addini, na Majalisar Masarautar, wadda aka bai wa manema labarai.

Da wannan, ana bukatar Musulmi su fara duban sabon watan Ramadan, tare da bayar da rahoto da zarar an gani, ga Hakimi ko Sarki mafi kusa, don tura bayanin ma Mai Alfarma Sarkin Musulmi.

Ramadan, wanda shi ne wata na tara a kalandar Musulunci, lokaci ne na azumi, wanda daya ne daga cikin shika shikai biyar na addinin Musulunci.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG