Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Zaben Kananan Hukumomi Zata Yi Wa 'Yan Takara Gwaji


Ofishin hukamar INEC
Ofishin hukamar INEC

Hukumar zaben kananan hukumomi a jihar Kano Najeriya ta ce zata gudanar da gwajin gano ta’ammali da ababen sanya maye ga dukkannin ‘yan takarar shugabancin kananan hukumomi da kansiloli a zaben da za a yi a watan gobe. Sai dai kasa da sa’o’i 24 da wannan furuci, fiye da mutane 300 masu muradin shiga takarar zaben suka kai kansu ofishin hukumar NDLEA na Kano domin yin gwajin. Wannan batu ya ja hankalin masu sharhi a jihar inda su ka yi tsokaci akan wannan batu.

A saurari rahoton Mahmud Ibrahim Kwari:

DRUGS TEST ON KANO LG ELECTIONS CANDIDATES.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG