Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

KALLABI: Shin Rashin Illimi Na Ruruta Karuwar Matsalar Shan Miyagun Kwayoyi Tsakanin Mata a Arewacin Najeriya? - Yuni 30, 2024


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

A shirin Kallabi na wanan makon zai duba yadda rashin ilimi ke tasiri akan matsalar karuwar shan miyagun kwayoyi tsakanin matan aure da zawarawa a arewacin Najeriya, inda a Makon da ya gabata Mata ‘yan fafatuka suka haska fitila kan matsalar a cikin shirin.

Batun shan miyagun gwayoyi da rahotanni ke nuni da cewa, yana kokarin shan kan al’umma a arewacin Najeriya da ya shafi matan aure da ‘yan mata, shirin kallabi ya karbi bakuncin Dr. Zarah Yusuf ‘yar fafatuka a Damaturu jihar Yobe, da kuma Aisha Moh’d Yakasai, shugabar kungiyar dake kula da tarbiyar matasa a jihar Kano, wadanda suka bayyana yadda rashin ilimi ke tasiri a ruruta wannan matsalar.

Sannan shirin zai ci gaba da tattauna da Helen Bako wadda ta shafe sama da shekaru 23 tana aikin daya jibanci kula da jin dadi da walwalar Al’umma musamman ma tsakanin Iyali a Amurka. Kuma shugabar wata kungiyar wanzar da zaman lafiya ta Mata da ake kira (Nigerian Women against Violence) dake aiki a ciki da wajen Najeriya, inda ta bayyana tsarin gudanar da aiki a kasashen Nahiyar Afrika da kuma yadda ya banbanta a Amurka.

Saurari cikakken shirin da Grace Alheri Abdu ta gabatar:

KALLABI: Shin Rashin Illimi Na Ruruta Karuwar Matsalar Shan Miyagun Kwayoyi Tsakanin Mata a Arewacin Najeriya? - Yuni 30, 2024
please wait

No media source currently available

0:00 0:22:26 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG