Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tinubu Ya Jajantawa Mutanen Da Ibtila’in Fashewar Iskar Gas Ya Rutsa Dasu A Ogun


Bola Tinubu
Bola Tinubu

WASHINGTON DC - Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya jajantawa mutanen da ibtila’in fashewar iskar gas ya rutsa dasu a yankin Ita-Oshin na Karamar Hukumar Abeokuta ta arewa dake jihar Ogun.

Fashewar wacce ta samu asali daga wata tankar dakon gas ta fantsama zuwa sassan yankin, al’amarin daya sabbaba asarar rayuka da dukiya.

A sanarwar da hadiminsa akan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale, ya fitar, Shugaba Tinubu ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Ogun game da afkuwar ibtila’in.

Ya kuma yabawa Gwamna Dapo Abiodun game da kokarinsa na shawo kan lamarin tare da dawo da kwanciyar hankula a yankin.

Shugaban kasar ya baiwa al’ummar jihar Ogun, musamman wadanda al’amarin ya shafa tabbacin samun agajinsa a wannan lokaci na alhin

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG