Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin Duniya Sun Bukaci Isra'ila Kada Ta Mayar Da Martani Ga Iran


Taron UN akan tashin hankalin da ke ci gaba a Gabas ta Tsakiya da kuma sabon harin Iran kan Isra’ila - Hedkwatar UN, New York Afrilu 14, 2024.
Taron UN akan tashin hankalin da ke ci gaba a Gabas ta Tsakiya da kuma sabon harin Iran kan Isra’ila - Hedkwatar UN, New York Afrilu 14, 2024.

Shugabannin duniya sun bukaci Isra'ila da kada ta mayar da martani bayan da Iran ta kai harin da ya hada da daruruwan jirage marasa matuka, da makamai masu linzami da kuma sauran makamai.

WASHINGTON, D. C. - Sakataren harkokin wajen Birtaniya David Cameron ya shaida wa BBC a ranar Litinin cewa, Birtaniya ba ta goyon bayan wani mayar da martani na ramuwar gayya, yayin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce Paris za ta yi kokarin shawo kan Isra'ila cewa kada ta mayar da martani domin hana karuwar rikicin.

David Cameron - UK
David Cameron - UK

Harin da Iran ta kai a ranar Asabar, kasa da makonni biyu bayan wani harin da ake zargin Isra’ila ta kai a Syria, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu jami’an Iran a wani ginin karamin ofishin jakadancin Iran, shi ne karon farko da Iran ta kaddamar da farmakin soji kai tsaye kan Isra’ila, duk kuwa da cewa sun dade suna kiyayya da ta shafe shekaru da dama ana yi tun lokacin juyin juya hali na 1979.

Kakakin sojin Isra'ila ya ce kashi 99 cikin 100 na makaman da Iran ta harba an dakile su.

Makaman roka da makamai marasa matuki da Iran ta harba kan Isra’ila, aka hanga daga Ashkelon
Makaman roka da makamai marasa matuki da Iran ta harba kan Isra’ila, aka hanga daga Ashkelon

Isra'ila da Iran suna zaman dar-dar da juna tsawon watanni shida tun da farkon yakin da Isra'ila ta fara da mayakan Hamas a zirin Gaza. Yakin ya barke bayan da kungiyar Hamas da ke samun goyon bayan Iran, suka kai wani mummunan hari a kan iyaka a ranar 7 ga watan Oktoba, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 1,200 a Isra'ila tare da yin garkuwa da wasu karin 250.

Bayan nan harin da Isra'ila ta kai a Gaza ya haifar da barna mai yawa tare da kashe mutane sama da 33,700, a cewar jami'an kiwon lafiya na yankin.

-AP

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG