Jirgin Boeing 777-300ER, mai dauke da fasinjoji 211 da ma'aikatan jirgin 18, ya sauka a Bangkok da karfe 3:45 na rana (0845 agogon GMT), kamfanin jirgin ya ce a cikin wani sakon Facebook.
"Abin da ke faruwa a Gaza ba kisan kare dangi ba ne, mun yi watsi da hakan," in ji Biden a wani taron watan al'adun Yahudawa na Amurka a fadar White House.
Babban mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ya nemi a kamo shugabannin Isra’ila da Hamas a ranar Litinin, wadanda suka hada da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, kan irin matakan da suka dauka a yakin da suka kwashe watanni bakwai ana yi.
Fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta bayyana a ranar Litinin cewa ta yi marhabin da sanarwar da mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ICC ya yi akan shugabannin Isra’ila da Hamas.
Nadin Mokhbar na wucin gadi na bukatar samun amincewar jagoran addinin kasar Ayatollah Ali Khamenei.
Hakan na faruwa ne yayin da Benny Gantz yake barazanar ajiye aikinsa na mamba a kwamitin yaki idan Isra'ila ba ta sauya yadda take tafiyar da yakin na Gaza ba.
Gidan talbijin na State TV bai fadi abin da ya haddasa hatsarin ba wanda ya auku a gabashin lardin Azerbaijin.
A halin da ake ciki, Isra'ila na kokarin yi wa birnin Rafah kawanya, suna masu cewa birnin shi ne mabuya ta karshe ga mayakan Hamas.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya sauka yau Alhamis a birnin Beijing domin gudanar da ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Sin, a wani mataki na nuna hadin kai tsakanin kasashen masu kama karya a yayin da Moscow ke ci gaba da kai sabbin hare hare a Ukraine.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a ranar Laraba ya yi watsi da sukarsa da ake yi cewa ba ya shirin fuskantar dahir a zirin Gaza bayan yaki, yana mai cewa ba zai taba yiwuwa a shirya wani yanayi a yankin Falasdinawa da ke fama da rikici ba har sai an fatattaki Hamas.
Taiwo ta rasu ne a watan Nuwamban shekarar 2023 sakamakon mumunan raunin da ta samu a kwakwalwar ta bayan afkuwar mumunan lamarin a gidan su da ke Newmarket.
Domin Kari
No media source currently available
Amurkawa da dama da za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Har yanzu matsalar cin hanci da rashawa ta na da girma sosai a kasashen nahiyar, ciki har da Ghana. A cewar hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar, kashi 20 cikin dari na kasafin kudin kasar ya na silalewa ne saboda matsalar cin hanci da rashawa.
A kowacce shekara, dubban ‘yan Najeriya su na kai rahoton almundahana ga hukumomi. A 2021, kimanin korafe-korafe dubu 140 ne a ka shigar, wanda shi ne lamari mafi yawa a cikin shekaru hudu, a cewar hukumar ta EFCC.
Amurkawa za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Wani matashi a garin Larabar Abasawa dake karamar hukumar Gezawa ya cinnawa wani masallaci wuta yayin da mutane suke sallar asubahi. Rundunar ‘yan sadan jihar ta ce mutumin ya zuba fetur ne, ya banka wuta, sannan ya rufe kofar masallacin. Kimanin mutane 35 ne suka samu raunukan sakamakon al'amarin.
Bayan kawancen soji dake tsakanin kasashen biyu, a yanzu haka kasar ta Rasha ta bullo da wani sabon tsari na koyar da harshen kasarta a makaratun Nijar. Yayin da wasu ‘yan Nijar ke alfahari da shirin, wasu kuwa jan hankalin hukumomin kasar suke yi a game da matsalar da za a iya samu.