Marasa rinjayi a Majalisar dokokin Ghana sun bayyana damuwarsu kan kalubalen da darajar kudin Ghana wato Sidi ke fuskanta da har yanzu aka gaza samar da mafita, suna masu gargadin cewa lamarin zai kara ta’azzara.
Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Olayemi Cardoso ya ce kayayyakin abincin da gwamnati take saya don rabawa mabukata na daga cikin dalilan da suke kara hauhawar farashin kayayyaki a kasar.
Najeriya ta samu jarin dalar Amurka miliyan 600 na samar da kayayyakin aiki a tashar jiragen ruwa daga kamfanin jigilar kayayyaki na kasar Denmark A.P. Moller-Maersk MAERSKb.CO, kamar yadda fadar shugaban kasar ta fitar ranar Lahadi.
A makon da ya gabata dan takarar Shugaban kasa a zaben 2023 karkashin babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar ya yi kira da a gudanar da binciken “gaggawa” kan zargin na Ningi.
Attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka, Aliko Dangote na shirin kafa wata kungiyar hada-hadar man fetur, mai yiwuwa a birnin Landan.
'Yan kasuwar canjin kudi da dama sun nuna rashin gamsuwa da soke lasisin sama da kamfanonin canji 4000 da babban bankin Najeriya CBN ya yi.
Babban Bankin Najeriya CBN ya soke lasisin wasu kamfanonin canjin kudi 4,173, cikin kimanin 5000 da ake da su.
A cewar masanin, lokaci ya yi da matasa za su kara mayar da hankalinsu kan koyon ilimin na'ura mai kwakwalwa wanda hakan zai ba su dama su yi aiki daga ko'ina a duniya.
Farashin hannun jari Access Holdings na Najeriya ya fadi da kaso 6.26 a yau yayin da masu hannun jari a kamfanin ke alhinin rasuwar Herbert Wigwe.
Kamfanin na Dangote ya kara da cewa har ya turawa EFCC wasu bayanai a mataki na farko, amma jami’an hukumar suka ki karbar bayanan suka kuma matsa cewa sai sun kai ziyara hedkwatar kamfanin.
An gudanar da taron karfafawa al’ummar zanguna kwarin gwiwar kasuwanci ko Zongo Startup Summit 2023, tare da yin kira ga matasa da su kasance masu halayen da suka dace, domin samun nasarar kasuwancinsu.
Wannan kudiri da Majalidsar ta Wakilai ta sa a gaba ya sa masana tattalin arziki bayyana ra'ayoyin mabanbanta
Domin Kari
No media source currently available
Amurkawa za su yi zabe a watan Nuwamba, batutuwan da suka shafi Afirka ba su dame su sosai ba. Sai dai masu sharhi na ganin duk wanda ya yi nasara a zaben, yana da jan aiki na dawowa kimar Amurka a nahiyar ta Afirka.
Wani matashi a garin Larabar Abasawa dake karamar hukumar Gezawa ya cinnawa wani masallaci wuta yayin da mutane suke sallar asubahi. Rundunar ‘yan sadan jihar ta ce mutumin ya zuba fetur ne, ya banka wuta, sannan ya rufe kofar masallacin. Kimanin mutane 35 ne suka samu raunukan sakamakon al'amarin.
Bayan kawancen soji dake tsakanin kasashen biyu, a yanzu haka kasar ta Rasha ta bullo da wani sabon tsari na koyar da harshen kasarta a makaratun Nijar. Yayin da wasu ‘yan Nijar ke alfahari da shirin, wasu kuwa jan hankalin hukumomin kasar suke yi a game da matsalar da za a iya samu.
Ma’aunin matsalar cin hanci da rashawa a Zambia ya nuna cewa kasar ta samu ci gaba a karon farko cikin shekaru goma, kamar yadda kungiyar Transparency International a kasar ta sanar. Hukumomi a kasar sun ce kwalliya ta fara biyan kudin sabulu a dagewar da suka yi wajen karfafa bin doka da oda.
A lokacin da Martha Ngoye take aiki a matsayin babbar jami’ar al’amuran shari’a a hukumar sufurin jiragen kasa ta Afirka ta Kudu, ta kwarmata badakalar kwangilolin gwamnati na miliyoyin kudi da aka bayar ba bisa ka’ida ba. Sai dai a maimakon a sakanya mata da alheri, sai aka kore ta a wurin aiki.
Kungiyoyin tabbatar da ka’ida a hada-hadar tattalin arziki a Malawi sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta magance wasu matsaloli da ke tattare da tsarin bayar da kwangiloli na kasar.Wani rahoto a 2021 ya nuna cewa harkokin bayar da kwangiloli na gwamnati a kasar suna dabaibaye da cin hanci da rashawa