Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dubban ‘Yan Kenya Sun Yi Zanga-zanga Akan Karin Haraji


Zanga-zangar karin haraji a Nairobi, Kenya
Zanga-zangar karin haraji a Nairobi, Kenya

'Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa da ruwa domin tarwatsa masu zanga-zanga a Nairobi babban birnin kasar Kenya da wasu biranen kasar a ranar Talata yayin da dubban mutane suka fantsama kan tituna a fadin kasar domin nuna adawa da shirin karin haraji

Rundunar ‘yan sandan ta kuma rufe majalisar, inda ‘yan majalisar ke tafka mahawara kan kudirin kara harajin, da kuma fadar shugaban kasa, wurin ofishin shugaban kasa da gidan sa yake.

Nairobi
Nairobi

Masu shirya zanga-zangar dai sun yi kira da a gudanar da zanga-zanga da kuma yajin aikin gama-gari na adawa da dokar harajin da fatan za a ci gaba na tsawon mako guda, lamarin da ya mayar da yunkurin da matasa ke yi a yanar gizo ya zama babban ciwon kai ga gwamnati.

Masu zanga-zangar sun kuma yi kira ga shugaba William Ruto da ya sauka daga karagar mulki.

Shugaban kasar Kenya, William Ruto
Shugaban kasar Kenya, William Ruto

Ruto ya lashe zaben da aka gudanar ne kusan shekaru biyu da suka gabata a kan wani tsarin da zai jagoranci talakawan Kenya masu aiki, amma ya tsinci kan shi tsakanin bukatun masu ba da lamuni kamar asusun lamuni na duniya IMF, wanda ke kira ga gwamnati da ta rage gibi, da kuma al'ummar da ke fama da tsadar rayuwa a kasar.

'Yan jaridar Reuters sun ce yayin da masu zanga-zangar suka gudanar da zanga-zanga a ranar Talata, 'yan sanda sun harba barkonon tsohuwa a yankin tsakiyar kasuwanci da kuma garin Kibera.

Daruruwan mutane kuma sun yi tattaki a kan titunan birnin Mombasa da ke gabar teku, a Kisumu, wani tashar jiragen ruwa a tafkin Victoria, da kuma sauran garuruwa, kamar yadda gidan talabijin na Kenya ya nuna.

'Yan sanda dai sun tarwatsa duk wadanda suka taru a titunan da ke kewayen majalisar kasar a birnin Nairobi.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG