Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

China Ta Yi Alkawarin Tallafawa Afirka Da Dala Biliyan 50


A cewar Shugaba Xi, za a bada fiye da rabin adadin kudaden a matsayin bashi, inda za a zuba dala biliyan 11 “cikin nau’ukan tallafi daban-daban” sannan a bayar da dala biliyan 10 ta hanyar karfafa gwiwar kamfanonin China su zuba jari.

A yau Alhamis, Shugaban China Xi Jinping ya dauki alkawarin tallafawa Afirka da fiye da dala biliyan 50 nan da shekaru 3 masu zuwa, inda ya sha alwashin yaukaka alaka da kasashen nahiyar a bangaren samar da kayayyakin more rayuwa da cinikayya yayin da yake jawabi a taro mafi girma da birnin Beijing ya karbi bakunci tun bayan annobar Korona.

A jawabinsa ga shugabannin yayin kaddamar da taron a birnin Beijing, Shugaba Xi ya yabawa kawancen kasar da Afirka.

Shugaban China Xi Jiping da shugabannin kasashen nahiyar Afirka
Shugaban China Xi Jiping da shugabannin kasashen nahiyar Afirka

Xi ya kara da cewa, “a shirye China take ta kyautata alaka da kasashen Afirka a fannonin masana’antu da noma da samar da kayayyakin more rayuwa da cinikayya da kuma zuba jari.

“Nan da shekaru 3 masu zuwa, gwamnatin China nada niyar bayar da tallafin kudaden da suka kai yuan biliyan 360 (kwatankwacin dala biliyan 50.7).

A cewar Shugaba Xi, za a bada fiye da rabin adadin kudaden a matsayin bashi, inda za a zuba dala biliyan 11 “cikin nau’ukan tallafi daban-daban” sannan a bayar da dala biliyan 10 ta hanyar karfafa gwiwar kamfanonin China su zuba jari.

Ya kuma dauki alkawarin taimakawa wajen “samar da akalla guraben aikin yi miliyan daya a nahiyar Afirka”.

Shugaban na China ya kuma sha alwashin bada agajin dala miliyan 141 a matsayin tallafi ga hukumomin soji a nahiyar Afirka.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG